Home General Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta...

Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta Kudu

Akalla mutane 30 ne aka kashe a fadan da aka yi a wani gari da ke arewacin Sudan ta Kudu wanda wasu gungun matasa ɗauke da makamai suka mamaye na wani dan lokaci bayan wani farmakin da suka kai na shanu, kamar yadda wani jami’in yankin ya sanar a jiya Alhamis.

Lamarin ya faru a yankin arewacin Ruweng a farkon mako lokacin da wasu matasa dauke da makamai suka sace raguna kafin jami’an tsaro su fatattake su, in ji Simon Chol Mialith, ministan yada labaran yankin.

Washegari, kamar yadda ya shaida wa AFP, kungiyar matasan ta dawo da yawa inda suka kai hari a garin Abiemnom.

Ministan ya kara da cewa, “matasa da jami’an tsaro sun yi kokarin kare birnin amma matasa dauke da makamai suka mamaye su.

A ranar Larabar da ta gabata ce Dakarun tsaron Sudan ta Kudu (SSPDF) suka fatattaki ‘yan kungiyar da ke dauke da makamai tare da samun kwanciyar hankali, in ji Mialith. “Akwai matattu talatin da kuma jikkata kusan arba’in,” ​​in ji shi, ba tare da yin karin bayani ba.

Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa wasu daga cikin wadanda aka kashe na kungiyar ne, amma kamfanin dillancin labaran AFP ya kasa tabbatar da wannan labarin.

Rikici tsakanin makiyaya da al’ummomin da ba sa zaman kashe wando dai ya zama ruwan dare a Sudan ta Kudu, sai dai wadannan al’amura na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin siyasa ya tsananta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp