Home General Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta...

Mutane da dama ne suka mutu a wani fada a Sudan ta Kudu

Akalla mutane 30 ne aka kashe a fadan da aka yi a wani gari da ke arewacin Sudan ta Kudu wanda wasu gungun matasa ɗauke da makamai suka mamaye na wani dan lokaci bayan wani farmakin da suka kai na shanu, kamar yadda wani jami’in yankin ya sanar a jiya Alhamis.

Lamarin ya faru a yankin arewacin Ruweng a farkon mako lokacin da wasu matasa dauke da makamai suka sace raguna kafin jami’an tsaro su fatattake su, in ji Simon Chol Mialith, ministan yada labaran yankin.

Washegari, kamar yadda ya shaida wa AFP, kungiyar matasan ta dawo da yawa inda suka kai hari a garin Abiemnom.

Ministan ya kara da cewa, “matasa da jami’an tsaro sun yi kokarin kare birnin amma matasa dauke da makamai suka mamaye su.

A ranar Larabar da ta gabata ce Dakarun tsaron Sudan ta Kudu (SSPDF) suka fatattaki ‘yan kungiyar da ke dauke da makamai tare da samun kwanciyar hankali, in ji Mialith. “Akwai matattu talatin da kuma jikkata kusan arba’in,” ​​in ji shi, ba tare da yin karin bayani ba.

Kafofin yada labaran cikin gida sun ruwaito cewa wasu daga cikin wadanda aka kashe na kungiyar ne, amma kamfanin dillancin labaran AFP ya kasa tabbatar da wannan labarin.

Rikici tsakanin makiyaya da al’ummomin da ba sa zaman kashe wando dai ya zama ruwan dare a Sudan ta Kudu, sai dai wadannan al’amura na zuwa ne a daidai lokacin da rikicin siyasa ya tsananta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp