Home General Kotu ta dakatar da gangamin magoya bayan Wike a Bayelsa Wike

Kotu ta dakatar da gangamin magoya bayan Wike a Bayelsa Wike

Wata babbar kotu a jihar Bayelsa ta dakatar da magoya bayan Ministan Abuja, Nyesom Wike daga shirya gangamin siyasa da suke shirin yi a jihar.

Kotun ta ce a dakata da gudanar da taron har sai ta saurara tare da yanke hukunci.

Asali dai an shirya gudanar da taron ne a birnin Yenagoa a ranar 12 ga watan Afrilun bana, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Mai shari’a I.A Uzakah ne ya yanke hukuncin mai lamba BYHC/YHC/CV/133/2025, bayan kwamishinan shari’a na jihar Biriyai Dambo ya shigar da ƙara.

Kotun ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 11 ga watan Afrilu.

Ana dai ta cacar-baki ne tsakanin gwamnatin jihar Bayelsa da magoya bayan Wike na jihar, inda magoya bayan ministan suka dage kai da fata sai sun shirya taron gangamin, shi kuma gwaman jihar ya ce allambaran ba a jiharsa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp