Home General Kotu ta dakatar da gangamin magoya bayan Wike a Bayelsa Wike

Kotu ta dakatar da gangamin magoya bayan Wike a Bayelsa Wike

Wata babbar kotu a jihar Bayelsa ta dakatar da magoya bayan Ministan Abuja, Nyesom Wike daga shirya gangamin siyasa da suke shirin yi a jihar.

Kotun ta ce a dakata da gudanar da taron har sai ta saurara tare da yanke hukunci.

Asali dai an shirya gudanar da taron ne a birnin Yenagoa a ranar 12 ga watan Afrilun bana, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Mai shari’a I.A Uzakah ne ya yanke hukuncin mai lamba BYHC/YHC/CV/133/2025, bayan kwamishinan shari’a na jihar Biriyai Dambo ya shigar da ƙara.

Kotun ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 11 ga watan Afrilu.

Ana dai ta cacar-baki ne tsakanin gwamnatin jihar Bayelsa da magoya bayan Wike na jihar, inda magoya bayan ministan suka dage kai da fata sai sun shirya taron gangamin, shi kuma gwaman jihar ya ce allambaran ba a jiharsa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp