Kotu ta dakatar da gangamin magoya bayan Wike a Bayelsa Wike

Wata babbar kotu a jihar Bayelsa ta dakatar da magoya bayan Ministan Abuja, Nyesom Wike daga shirya gangamin siyasa da suke shirin yi a jihar.

Kotun ta ce a dakata da gudanar da taron har sai ta saurara tare da yanke hukunci.

Asali dai an shirya gudanar da taron ne a birnin Yenagoa a ranar 12 ga watan Afrilun bana, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.

Mai shari’a I.A Uzakah ne ya yanke hukuncin mai lamba BYHC/YHC/CV/133/2025, bayan kwamishinan shari’a na jihar Biriyai Dambo ya shigar da ƙara.

Kotun ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar 11 ga watan Afrilu.

Ana dai ta cacar-baki ne tsakanin gwamnatin jihar Bayelsa da magoya bayan Wike na jihar, inda magoya bayan ministan suka dage kai da fata sai sun shirya taron gangamin, shi kuma gwaman jihar ya ce allambaran ba a jiharsa ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 14 hours 58 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 16 hours 39 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com