Home General Hedkwatar tsaron Najeriya ta magantu kan ceto Janar Tsiga

Hedkwatar tsaron Najeriya ta magantu kan ceto Janar Tsiga

Hedkwatar tsaron Najeriya ta ce babu kuɗin fansa da aka biya kafin sakin tsohon shugaban Hukumar yi wa Ƙasa Hidima a Najeriya NYSC, Manjo Janar Mahrazu Tsiga, mai ritaya daga hannun ƴanbindiga.

Wata sanarwa da mai magana da yawun hedkwatar tsaron Birgediya-Janar Tukur Gusau ya fitar, ya ce sojoji sun yi amfani da dabarun karfi da kuma bayanan sirri wajen ceto Janar Tsiga.

“Tun bayan sace Janar Tsiga ranar 7 ga watan Fabrairu, sojoji ba su yi ƙasa a gwiwa ba. Sun kai samame ta sama da kuma ƙasa a ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Faskari da kuma Kankara inda ake kyautata zaton masu garkuwan sun ajiye shi,” a cewar Tukur Gusau.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin sun yi ta aiki tukuru babu dare ba rana wajen nema da kuma ceto tsohon shugaban na NYSC.

An dai yi garkuwa da shi ne ranar 5 ga watan Fabrairu, a garin mahaifarsa ta Tsiga da ke karamar hukumar Bakori na jihar Katsina – tare da wasu mutum 13.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp