Home General Za a ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da...

Za a ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da naira

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da kuɗin naira.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin kuɗi ta tarayya ta fitar a shafinta na X ranar Laraba.

Ma’aikatar ta ce tsarin, wanda majalisar zartaswa ta fara amincewa da shi, wani daɗaɗɗen yunkuri ne da aka ɗauki tsawon lokaci ana tsara shi.

A cewar ma’aikatar, masu ruwa da tsaki sun nuna goyon bayansu da kuma tabbatar da ganin tsarin na sayar da ɗanyen mai ga matatu a naira ya tafi daidai.

Tsarin wanda ya buƙaci cinikayyar ɗanyen mai a kuɗin naira, an yi shi ne da zimmar ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar da inganta tace mai a ƙasar da kuma daidaita ƙudin ƙasashen waje ta hanyar rage buƙatar dala a cinikayyar ɗanyen mai.

Ma’aikatar ta ƙara da cewa wannan tsari zai kuma janyo hankalin masu zuba jari a ɓangaren tace ɗanyen mai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp