Home General Gwamnoni ku dauki aniyar hidimtawa Al’umma – buhari

Gwamnoni ku dauki aniyar hidimtawa Al’umma – buhari

Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce kadarar da ya mallaka tun kafin ya hau mulki ba ta ƙaru ba har bayan saukarsa daga mulki a watan Mayun 2023.

Cikin wata sanarwa da kakakin tsohon shugaban, Mallam Garba Shehu ya fitar ya ce Buhari ya bayyana haka ne a lokacin ganawa da gwamnonin APC da suka kai masa ziyara a gidansa da ke Kaduna.

Tsohon shugaban ya shawarci gwamnonin na APC su rungumi aniyar hidimta wa al’umma, yana mai cewa shugabanci cike yake da tarin ƙalubale da kuma dama, kuma haɗa abubuwan biyu ne zai ciyar da ƙasa gaba.

Haka Muhammadu Buhari ya bayyana ƙwarin gwiwarsa kan gwamnonin na APC da irin nasarar da ya ce an samu samu a jihohinsu.

Tsohon shugaban ya kuma gode wa gwamnatin Tinubu saboda gyara masa gidansa na Kaduna.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, wanda kuma shi ne gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya ce ƙungiyar tasu ta kai wa tsohon shugaban ziyarar barka da sallah, tare da bayyana godiyarsu da girmamawa ga tsohon shugaban kan gudunmowar da ya bayar ga dimokradiyya.

Tsohon shugaban ya gode wa gwamnonin kan ziyarar, yana mai cewa yayin da ya yi aiki da wasu wasun kuma sabbi ne a gare shi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp