Home General Gwamnoni ku dauki aniyar hidimtawa Al’umma – buhari

Gwamnoni ku dauki aniyar hidimtawa Al’umma – buhari

Tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce kadarar da ya mallaka tun kafin ya hau mulki ba ta ƙaru ba har bayan saukarsa daga mulki a watan Mayun 2023.

Cikin wata sanarwa da kakakin tsohon shugaban, Mallam Garba Shehu ya fitar ya ce Buhari ya bayyana haka ne a lokacin ganawa da gwamnonin APC da suka kai masa ziyara a gidansa da ke Kaduna.

Tsohon shugaban ya shawarci gwamnonin na APC su rungumi aniyar hidimta wa al’umma, yana mai cewa shugabanci cike yake da tarin ƙalubale da kuma dama, kuma haɗa abubuwan biyu ne zai ciyar da ƙasa gaba.

Haka Muhammadu Buhari ya bayyana ƙwarin gwiwarsa kan gwamnonin na APC da irin nasarar da ya ce an samu samu a jihohinsu.

Tsohon shugaban ya kuma gode wa gwamnatin Tinubu saboda gyara masa gidansa na Kaduna.

Shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, wanda kuma shi ne gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma ya ce ƙungiyar tasu ta kai wa tsohon shugaban ziyarar barka da sallah, tare da bayyana godiyarsu da girmamawa ga tsohon shugaban kan gudunmowar da ya bayar ga dimokradiyya.

Tsohon shugaban ya gode wa gwamnonin kan ziyarar, yana mai cewa yayin da ya yi aiki da wasu wasun kuma sabbi ne a gare shi.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp