Home General Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Kungiyar Zago Akida ta jihar Kano ta kai ziyarar ga mataimakin shugaban majalisar dattijan Nijeriya Sanata Barau I Jibril Maliya.

Kungiyar karkashin jagorancin shugabanta Mukhtar BBA Gwammaja ta Kai ziyarar ne a gidan sanata dake birnin tarayyar Nijeriya Abuja a ranar Laraba bisa abin da ta kira managarta ayyukan da sanata yake yiwa Al’ummar jihar kano da kasa baki dai.

Da yake jawabi sanata Barau ya bayyana Jagoran kungiyar ta Zago Akida Marigayi Amb. Hon Alhaji Ahmadu Haruna Zago matsayin jajirtaccen ɗan siyasa bisa irin gudunmawar da ya bashi a fannin siyasar gidan sa.

Sanata Barau ya bayyana cewa “Nima dan Zago Akida ne, tabbas anyi babban rashi na Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago, amma Zago Akida ba marainiya nace, don zan zame mata gata wajen yi mata dukkan abin da take bukata.

Daga bisani sanata Barau ya Gwangwaje kungiya tlda kyautar kudi har Naira Miliyan 5 tare da bata kyautar mota gami da daukar alkawarin gami da daukar alkawarin samarwa da kungiyar dukkan abinda take bukata.

Da yake jawabi tun da bari shugaban kungiyar Mukhtar B.A Gwammaja ya godewa sanata Barau bisa karancin da ya nunawa ƙungiyar da kuma Marigayi Ambasada Ahmadu Haruna Zago.

Ya kuma bayyana cewa kungiyar zata cigaba da taimakawa kokarin sanatan ta ko wacce fuska.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp