Home General Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Kungiyar Zago Akida ta jihar Kano ta kai ziyarar ga mataimakin shugaban majalisar dattijan Nijeriya Sanata Barau I Jibril Maliya.

Kungiyar karkashin jagorancin shugabanta Mukhtar BBA Gwammaja ta Kai ziyarar ne a gidan sanata dake birnin tarayyar Nijeriya Abuja a ranar Laraba bisa abin da ta kira managarta ayyukan da sanata yake yiwa Al’ummar jihar kano da kasa baki dai.

Da yake jawabi sanata Barau ya bayyana Jagoran kungiyar ta Zago Akida Marigayi Amb. Hon Alhaji Ahmadu Haruna Zago matsayin jajirtaccen ɗan siyasa bisa irin gudunmawar da ya bashi a fannin siyasar gidan sa.

Sanata Barau ya bayyana cewa “Nima dan Zago Akida ne, tabbas anyi babban rashi na Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago, amma Zago Akida ba marainiya nace, don zan zame mata gata wajen yi mata dukkan abin da take bukata.

Daga bisani sanata Barau ya Gwangwaje kungiya tlda kyautar kudi har Naira Miliyan 5 tare da bata kyautar mota gami da daukar alkawarin gami da daukar alkawarin samarwa da kungiyar dukkan abinda take bukata.

Da yake jawabi tun da bari shugaban kungiyar Mukhtar B.A Gwammaja ya godewa sanata Barau bisa karancin da ya nunawa ƙungiyar da kuma Marigayi Ambasada Ahmadu Haruna Zago.

Ya kuma bayyana cewa kungiyar zata cigaba da taimakawa kokarin sanatan ta ko wacce fuska.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp