Home General Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Nima ɗan ƙungiyar Zago Akida ne -Sanata Barau

Kungiyar Zago Akida ta jihar Kano ta kai ziyarar ga mataimakin shugaban majalisar dattijan Nijeriya Sanata Barau I Jibril Maliya.

Kungiyar karkashin jagorancin shugabanta Mukhtar BBA Gwammaja ta Kai ziyarar ne a gidan sanata dake birnin tarayyar Nijeriya Abuja a ranar Laraba bisa abin da ta kira managarta ayyukan da sanata yake yiwa Al’ummar jihar kano da kasa baki dai.

Da yake jawabi sanata Barau ya bayyana Jagoran kungiyar ta Zago Akida Marigayi Amb. Hon Alhaji Ahmadu Haruna Zago matsayin jajirtaccen ɗan siyasa bisa irin gudunmawar da ya bashi a fannin siyasar gidan sa.

Sanata Barau ya bayyana cewa “Nima dan Zago Akida ne, tabbas anyi babban rashi na Amb. Alhaji Ahmadu Haruna Zago, amma Zago Akida ba marainiya nace, don zan zame mata gata wajen yi mata dukkan abin da take bukata.

Daga bisani sanata Barau ya Gwangwaje kungiya tlda kyautar kudi har Naira Miliyan 5 tare da bata kyautar mota gami da daukar alkawarin gami da daukar alkawarin samarwa da kungiyar dukkan abinda take bukata.

Da yake jawabi tun da bari shugaban kungiyar Mukhtar B.A Gwammaja ya godewa sanata Barau bisa karancin da ya nunawa ƙungiyar da kuma Marigayi Ambasada Ahmadu Haruna Zago.

Ya kuma bayyana cewa kungiyar zata cigaba da taimakawa kokarin sanatan ta ko wacce fuska.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp