Home General Nijeriya ta kama hanyar durkushewa- Peter Obi

Nijeriya ta kama hanyar durkushewa- Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Najeriya na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi ya yi kira ga ƴan hamayya su riƙa magana kan abin da ya kira shugabanci maras kyau da ƙasar ke fuskanta, yayin da ya ce ta kama hanyar durƙushewa.

Yayin da yake jawabi a taron kwamitin zartaswa na jam’iyyar a Abuja ranar Laraba, Mista Obi ya koka kan yawan talaucin da halin matsi da ake fama da shi a ƙasar.

Ya ce abubuwa na ƙara lalacewa a ƙasar, kuma lokaci ya yi da za a haɗa kai wajen yin abin da ya dace, farawa daga jam’iyyarsa ta LP.

“Dole mu yi magana idan abubuwa suka lalace, Najeriya na kan hanyar durƙushewa, alƙaluma a bayyane suke, mutane da yawa na ƙara talaucewa, mutanen da a baya ke cin abinci mai kyau, yanzu sun koma mabarata…”.

“A baya idan na zo nan, mutane kan riƙa tambayata abin da nake son ci ko sha domin su kawo min, amma yanzu babu wanda yake tambayata, wannan na nuna halin talaucin da ƙasar nan ke ciki, don haka ya kamata mu tashi tsaye mu hada kai don yin gyara,” in ji Mista Obi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp