Home General Matatar Dangote ta rage farashin man fetur

Matatar Dangote ta rage farashin man fetur

Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da rage farashin litar man fetur da take sayar wa ƴan kasuwa masu gidajen mai zuwa naira 865 daga naira 880.

Tashar Channels ce ta ruwaito hakan, inda ta ce wata majiya ce daga matatar ta tabbatar mata da rage farashin a ranar Alhamis.

Ragin farashin ya zo ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin matatar Dangote da ministan kuɗin Najeriya, Wale Edun a ranar Talata.

Bayan taron ne gwamnatin Najeriya ta ce yarjejeniyar sayar wa Dangote ɗanyen mai da naira na nan, kuma za a cigaba da amfani da ita bayan a baya kamfanin NNPCL ya sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar.

Da wannan matakin ne ake sa ran gidajen man fetur da suke da yarjejeniya da matatar Dangote irin su MRS da Ardova da Heyden da sauransu za su rage farashin litar man fetur ɗinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp