Home General Za a ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da...

Za a ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da naira

Matatar Dangote

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da kuɗin naira.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin kuɗi ta tarayya ta fitar a shafinta na X ranar Laraba.

Ma’aikatar ta ce tsarin, wanda majalisar zartaswa ta fara amincewa da shi, wani daɗaɗɗen yunkuri ne da aka ɗauki tsawon lokaci ana tsara shi.

A cewar ma’aikatar, masu ruwa da tsaki sun nuna goyon bayansu da kuma tabbatar da ganin tsarin na sayar da ɗanyen mai ga matatu a naira ya tafi daidai.

Tsarin wanda ya buƙaci cinikayyar ɗanyen mai a kuɗin naira, an yi shi ne da zimmar ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar da inganta tace mai a ƙasar da kuma daidaita ƙudin ƙasashen waje ta hanyar rage buƙatar dala a cinikayyar ɗanyen mai.

Ma’aikatar ta ƙara da cewa wannan tsari zai kuma janyo hankalin masu zuba jari a ɓangaren tace ɗanyen mai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp