Home General Za a ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da...

Za a ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da naira

Matatar Dangote

Gwamnatin Tarayya ta ce za ta ci gaba da sayar wa matatun mai ɗanyen mai da kuɗin naira.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin kuɗi ta tarayya ta fitar a shafinta na X ranar Laraba.

Ma’aikatar ta ce tsarin, wanda majalisar zartaswa ta fara amincewa da shi, wani daɗaɗɗen yunkuri ne da aka ɗauki tsawon lokaci ana tsara shi.

A cewar ma’aikatar, masu ruwa da tsaki sun nuna goyon bayansu da kuma tabbatar da ganin tsarin na sayar da ɗanyen mai ga matatu a naira ya tafi daidai.

Tsarin wanda ya buƙaci cinikayyar ɗanyen mai a kuɗin naira, an yi shi ne da zimmar ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar da inganta tace mai a ƙasar da kuma daidaita ƙudin ƙasashen waje ta hanyar rage buƙatar dala a cinikayyar ɗanyen mai.

Ma’aikatar ta ƙara da cewa wannan tsari zai kuma janyo hankalin masu zuba jari a ɓangaren tace ɗanyen mai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp