Matatar man fetur ta Dangote ta sanar da rage farashin litar man fetur da take sayar wa ƴan kasuwa masu gidajen mai zuwa naira 865 daga naira 880.
Tashar Channels ce ta ruwaito hakan, inda ta ce wata majiya ce daga matatar ta tabbatar mata da rage farashin a ranar Alhamis.
Ragin farashin ya zo ne bayan wata tattaunawa da aka yi tsakanin matatar Dangote da ministan kuɗin Najeriya, Wale Edun a ranar Talata.
Bayan taron ne gwamnatin Najeriya ta ce yarjejeniyar sayar wa Dangote ɗanyen mai da naira na nan, kuma za a cigaba da amfani da ita bayan a baya kamfanin NNPCL ya sanar da kawo ƙarshen yarjejeniyar.
Da wannan matakin ne ake sa ran gidajen man fetur da suke da yarjejeniya da matatar Dangote irin su MRS da Ardova da Heyden da sauransu za su rage farashin litar man fetur ɗinsu.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1485 days 21 hours 23 minutes 40 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1467 days 23 hours 5 minutes 5 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com