Home General Kwamitin yaƙi da dabanci a Kano ya ce ya samu nasarar kama...

Kwamitin yaƙi da dabanci a Kano ya ce ya samu nasarar kama ɓatagari sama da 400

A jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, kwamitin kar-ta-kwana kan yaƙi da ayyukan daba da dawo da zaman lafiya da gyaran halin matasa, ya sanar da kama ɓata-gari fiye da 400.

Kwamitin ya ce daga cikin waɗanda aka kama ɗin, an yankewa kashi 70 cikin 100 a cikinsu hukunci.

Matsalar daba da ƙwacen waya dai, sun sa jama’a a Kano na rayuwa cikin firgici tare da ƙauracewa fitar dare da kuma yin taka tsan-tsan da rana kasancewar harin daba na iya rutsawa da mutum a kowane lokaci.

Dr Yusuf Ibrahim Kofarmata shi ne shugaban kwamitin kuma ya ce zuwa yanzu sun samu nasarorin da aka daɗe ba a samu ba.

Ya ce, “aiki ne babba, amma suna aiki sosai domin shiga lungu da saƙo tare da taimakon jami’an tsaro. Kuma muna da kotun ta fi da gidanka, inda muke yanke hukunci nan take

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp