Rahotannin daga jihar Zamfara a arewa maso yammacin Nijeriya na bayyana cewa wasu da ake zargin ƴan bindiga ne sun Kai hari ƙauyen biya aiki dake karamar hukumar tsafe ta jihar Zamfara, in da suka lalata akalla gidaje 10 da asibiti gami da masallacin juma’a .
Idan za a iya tunawa a baya bayan nan ƴan bindigar sun kai wani hari ina da suka bankawa gidaje da masallaco gami da kayan abinci wuta a wani hari da suka kai.
Read Also:
Harin ya auku ne da misalin karfe 8:00 na yammacin ranar asabar, wanda ake kyautata zaton mayakan dake karkashin dan ta’adda adamu Aliero ne suka kai.
Wata majiya ta shaidawa jaridar Emergency Digest cewa harin na matsayin ramuwar gayya bisa kisan Kanin Aliero wato Isuhu Yellow, da Dan sa na cikin sa a wani harin kwantan bauna da jamián tsaro suka yi a yankin Keta makwannin uku da suka gabata.
Shaidar gani da ido sun tabbatar da cewa ýan taáddan sun tasamma garin ne tare da bankawa abubuwan wuta ba tare da sun yi garku wa da kowa ba.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 9 hours 33 minutes 53 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 11 hours 15 minutes 18 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com