PDP ta ce ba za ta yi haɗaka da kowa ba

Gwamnonin babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a Najeriya sun nisanta kansu da yunƙurin haɗaka tsakanin jam’iyyarsu da wasu jam’iyyun siyasa.

Ƙungiyar gwamnonin ƙarƙashin gwamnan Bauchi Bala Mohammed ta ce ba za ta haɗe da wata jam’iyya ba da nufin tunkarar zaɓen 2027.

“Ba za mu shiga wata haɗaka ba da kowa da nufin tunkarar zaɓen 2027,” kamar yadda ƙungiyar gwamnonin PDP ta bayyana a sanarwar da ta fitar bayan taron da suka gudanar a Ibadan jihar Oyo.

Wannan dai ya ci karo da iƙirarin tsohon ɗantakarar jam’iyyar kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alhaji Atiku Abubakar a kwanakin baya inda ya ce suna yunƙurin ƙulla haɗaka da wasu jam’iyyu.

Sanarwar gwamnonin PDP ya nuna akwai saɓanin ra’ayi tsakanin ɓangarensu da na Atiku Abubakar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 9 hours 4 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 10 hours 46 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com