Ƴar Majalisar Dattawan Najeriya, mai wakilitar Kogi ta Tsakiya, Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan – da aka dakatar – ta yi kira ga babban sifeton ƴansandan ƙasar, ya mayar mata da jami’an tsaronta da aka janye mata lokacin da majalisa ta dakatar da ita.
Kiran na zuwa ne bayan da wasu mahara suka auka wa gidan kakanninta da ke jihar Kogi ranar Talatar da ta gabata.
Jaridun Najeriya sun ambato wata sanarwa da ofishin yaɗa labaran ƴar majalisar ya fitar, na cewa an kai harin ne a lokacin da ƙaninta ya je garin domin duba wani aikin mazaɓu da Natasha ke gudanarwa a garinta na Obeiba-Ihima.
Sanata Natasha ta yi zargin cewa ita aka ƙudiri aniyar kai wa harin, tana mai cewa maharan sun kai harin ne saboda a tunaninsu tana gidan.
Harin ya lalata wasu ɓangarorin gidan, wanda ƴar majalisar ta ce na kakanta ne.
To sai dai jami’an tsaro sun yi asarar daƙile harin, kamar yadda ta yi ƙarin haske.
A watan da ya gabata ne dai Majalisar Dattawan Najeriyar ta dakatar da ƴar majalisar tsawo wata shida, tare da tsayar da alawus-alawus da ake ba ta da jami’an tsaron da ke ba ta kariya, saboda zargin rashin ɗa’a.
Dakatarwar na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan ta zargi Shugaban Majalisar Dattawan Ƙasar, Sanata Godswill Akpabio da yunƙurin cin zarafi na lalata da amfani da ofishinsa wajen tursasawa da kuma daƙile mata aikinta.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 9 hours 26 minutes 36 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 11 hours 8 minutes 1 second
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com