Home General Ba a hana Kashim Shettima shiga Villa ba – Fadar Shugaban Najeriya

Ba a hana Kashim Shettima shiga Villa ba – Fadar Shugaban Najeriya

Fadar shugaban Najeriya, ta musanta wasu rahotonnin da ke zargin cewa an hana mataimakin shugaban ƙasar, Kashim Shettima shiga fadar shugaban ƙasar ta Villa.

A ƴan kwanakin nan an yi ta yaɗa jita-jitar cewa jami’an tsaro sun hana mataimakin shugaban ƙasar shiga fadar shugaban ƙasar.

To sai dai cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasar, da ke aiki da ofishin mataimakin shugaban ƙasar, Stanley Nkwocha ya fitar, ya ce labarin ba shi da tushe balle makama, ”ƙarya ce tsagwaronta da aka shirya domin nuna wa jama’a cewa akwai saɓani tsakanin manyan jami’an gwamnatin”.

”An shirya wannan labarin ƙarya ne domin haddasa ruɗani da saɓani a fadar shugaban ƙasa, haka kuma labari ne da ke son haddasa ruɗani a zukatan ƴanƙasa”, in ji sanarwar.

Fadar shugaban ƙasar ta ce ta fahimci masu yaɗa labaran ƙarya ne ke son raba kyakkyawar alaƙar da ke tsakanin shugaban ƙasar da mataimakin nasa, kuma haƙarsu ba za ta cimma ruwa ba, kamar yadda fadar ta bayyana.

Sanarwar ta ce matamakin shugaban ƙasar na mayar da hankalinsa kan ayyukan da ke gabansa na tallafa wa shugaban ƙasa wajen ciyar da Najeriya gaba, don haka ba ma shi da lokacin ɓatawa.

Daga ƙarshe sanarwar ta yi kira ga al’umma su yi watsi da labaran da suka fito da majiyoyi marasa tushe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp