Akwai ƴanƙasar waje da ke kai hari a Benue – Hyacinth Alia

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

Gwamnan jihar Benue da ke tsakiyar Najeriya, Hyacinth Alia ya yi zargi cewa maharan da suka kai hari jihar ba ƴan Najeriya ba ne.

Gwamnan ya faɗi hakan ne a wani shirin gidan talabijin na Channels, inda ya ce maharan na magana ne da wata irin Hausa da Fulatanci wanda ba irinsu ake yi a ƙasar ba.

“Waɗannan mutanen sun zo ne a shirye da makamansu da bindigogi ƙirar AK-47 da 49. Kuma ba su yi kama da ƴan Najeriya ba, ba sa magana kamar yadda muke yi, Hausarsu ba irin ta mu ba ce. “

Inda ya ƙara da cewa daga bayanan sirrin da suka samu daga mazauna yankunan da aka kai hare-hare, ya nuna cewa maharan ƴanƙsar waje ne.

Hakan na zuwa ne bayan wata ziyarar nuna alhini da mai baiwa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ya kai jihar.

Inda ya bai wa al’umomin jihar tabbataci kan matakan da ya ce gwamnatin na ɗauka domin magance matsalar tsaro a ƙasar.

Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da ake zargin wasu ƙungiyoyin ƴanbindiga na ƙasashen waje na kai hari wasu sassan ƙasar.

Kamar ƙungiyar Lakurawa da ke kai hare-hare a jihohin Sokoto da Zamfara da ke arewa-maso-yammacin ƙasar.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 8 hours 54 minutes 35 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 10 hours 36 minutes 0 second

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com