Home General Tinubu zai gana da shugabannin tsaro a Najeriya

Tinubu zai gana da shugabannin tsaro a Najeriya

Rahotanni a Najeriya na nuna cewa, shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu na shirin yin wata ganawa da hafsoshin tsaron ƙasar kan kashe-kashe a jihohin Filato da Benue da wasu sassan ƙasar.

Ganawar na zuwa ne bayan komawar shugaba Tinubu Najeriyar, bayan kwashe makonni biyu yana ziyarar aiki a Paris, babban birnin Faransa.

Ana sa ran ganawar za ta sake duba ƙarin tashin hankalin da ake samu da kuma matakan magance su.

Hakan na zuwa ne a yayin da gwamnatin ƙasar ke ɗora laifin ƙarin kashe-kashen da ake samu a kan gwamnonin jihohi.

Gwamnatin tarayyar na ɗora alhakin hakan kan rashin sanya kuɗaɗe kamar yadda ya kamata a cibiyoyin tsaron da ke jihohi duk da ɗumbin kuɗaɗen da ake warewa domin yin hakan.

Matsalar tsaro na ci gaba da zama babban ƙalubale ga hukumomin tsaro a ƙasar, lamarin da ke sanadiyyar mutuwar dubban rayuka.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp