Home General hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta fara raba kayan aikin...

hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta fara raba kayan aikin hajjin bana

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano dake Arewa maso yammacin Nijeriya ta fara raba kayan aikin hajjin bana ga maniyyata.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Jami’in Yada Labarai da Hulda da Jama’a na hukumar Sulaiman A. Dederi ya fita kuma aka raba manema labarai a jihar.

sanarwar ta ce Darakta Janar na Hukumar , Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya fara rabon muhimman kayayyakin aikin Hajji ga alhazan jihar da za su tafi kasa mai tsarki.

Alhaji Lamin Rabi’u ya bukaci dukkan masu shirin zuwa aikin Hajji da su yi amfani da kayan da aka raba yadda ya kamata, tare da kaucewa daukar wasu kayayya da hukumar kasar Saudi Arabia ta haramta

Haka kuma, ya umurci dukkan alhazai da su tuntuɓi jami’an aikin Hajji na kananan hukumominsu domin karɓar kayayyakin.

Bugu da ƙari, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta Najeriya, ta hannun Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON), da ta sake duba batun amfani da katin ATM wajen bayar da kudin alhazai. Ya jaddada bukatar bayar da kuɗaɗen tafiya (BTA) a matsayin kuɗi na hannu domin sauƙaƙa wa alhazai samun damar amfani da su.

A nasa bangaren, Shugaban Majalisar, Daraktoci na hukumar Alhaji Yusif Lawan, ya shawarci alhazan da su yi amfani da kayan da aka raba yadda ya dace.

Kayayyakin da ake rabawa sun haɗa da: jakunkunan hannu, kayan suttura na maza da na mata, hijabai, zobunan hannu , da kananan jakunkuna domin ajiye kuɗi da muhimman takardu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp