Home General hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta fara raba kayan aikin...

hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta fara raba kayan aikin hajjin bana

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano dake Arewa maso yammacin Nijeriya ta fara raba kayan aikin hajjin bana ga maniyyata.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da Jami’in Yada Labarai da Hulda da Jama’a na hukumar Sulaiman A. Dederi ya fita kuma aka raba manema labarai a jihar.

sanarwar ta ce Darakta Janar na Hukumar , Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa, ya fara rabon muhimman kayayyakin aikin Hajji ga alhazan jihar da za su tafi kasa mai tsarki.

Alhaji Lamin Rabi’u ya bukaci dukkan masu shirin zuwa aikin Hajji da su yi amfani da kayan da aka raba yadda ya kamata, tare da kaucewa daukar wasu kayayya da hukumar kasar Saudi Arabia ta haramta

Haka kuma, ya umurci dukkan alhazai da su tuntuɓi jami’an aikin Hajji na kananan hukumominsu domin karɓar kayayyakin.

Bugu da ƙari, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta Najeriya, ta hannun Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON), da ta sake duba batun amfani da katin ATM wajen bayar da kudin alhazai. Ya jaddada bukatar bayar da kuɗaɗen tafiya (BTA) a matsayin kuɗi na hannu domin sauƙaƙa wa alhazai samun damar amfani da su.

A nasa bangaren, Shugaban Majalisar, Daraktoci na hukumar Alhaji Yusif Lawan, ya shawarci alhazan da su yi amfani da kayan da aka raba yadda ya dace.

Kayayyakin da ake rabawa sun haɗa da: jakunkunan hannu, kayan suttura na maza da na mata, hijabai, zobunan hannu , da kananan jakunkuna domin ajiye kuɗi da muhimman takardu.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp