Mataimakain shugaban hukumar da ke lura da zirga-zirgar ababan hawa ta jihar Kano, KAROTA, Alhaji. Auwal Shuáibu Aranposu, ya bayar da tallafin maganguna ga asibitin hukumar domin inganta walwala da jin dadin ma’aikata.
Aranposu ya bayyana hakan ne yayin da yake ganawa da manema labarai, in da ya ce hakan na matsayin wani mataki na lura gami da inganta lafiyar jami’an hukumar, wadanda mafi yawan ayyukansu suna yi ne akan titinan jihar wajen dake da hadari.
Read Also:
Ya kuma kara da jan hankalin jami’an hukumar wajen kara lura a lokacin da suke tsaka da gudanar da aiki, sannan ya bukaci su da su yi amfani da asibitin yadda ya kamata.
Haka kuma ya bukaci malaman lafiyar da ke asibiti su yi amfani da magungunan yadda ya dace domin amfanin ma’aikatan hukumar.
Haka kuma ya kara tabbatarwa da jami’an irin yunkurin da hukumar ke yi waje ganin ta kare lafiya da rayukan dakarunta a dukkan in da suka sami kan su.
Daga bisani Aranposu ya yaba da kokarin jami’an wajen jajircewarsu a yayin da suke gudanar da ayyukansu, in da ya bukaci da su dore da hakan domin cigaban hukumar da jihar Kano.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 7 hours 41 minutes 0 second,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 9 hours 22 minutes 25 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com