Fitaccen attajirin Nahiyar Afirka Aliko Dangote ya ce zai samu kuɗin shiga a dukkanin hada-hadar kasuwancisa da ta kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa, dukda yadda harajin Amurka zai shafi kamfanoninshi.
Shugaban rukunin kamfanonin na Dangote ya ce kasuwancinsa da suka haɗa da matatar man fetur mai ƙarfin tace ganga dubu 650 a kullum zai ƙaru da dala biliyan 5 a shekarar 2026.
Adadin kuɗin shigar kamfanonin na Dangote dai a wannan shekarar ya kai dala biliyan 25 abin da ke nufin idan an samu ƙarin dala biliyan 5 zai kama dala biliyan 30 a baɗi.
Read Also:
Shugaban Amurka Donlad Trump ya ware fannin mai da gas daga ƙarin haraji abin da ya sa matatar Dangote ci gaba da shigar da mai a ƙasar. Baya ga haka Dangote na kai taki ƙasar ta Amurka.
Adadin harajin shigar da kaya da Najeriya ke biyan Amurka ya yi ƙasa da kashi 16 idan aka kwatanta da wanda Algeria ke biyan ƙasar, abin da ya bai wa ƙasar damar hada-hadar kasuwanci fiye da Algeria.
Dangote ya ce ya damu da harajin da Amurka ta sanya, saboda kashi 37 na takin da yake sayarwa na Urea yana zuwa Amurka ne. sai dai sun yi sa a ita ƙasar Algeria an ƙaƙaba mata kashi 30 na haraji.
A gefe guda kuma ana hasashen Dangote zai zama babban mai fitar da siminti a nahiyar Afirka a shekara mai zuwa, inda zai iya kere ƙasar Masar.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 6 hours 54 minutes 37 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 8 hours 36 minutes 2 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com