Home General Tinubu zai gana da kamfanonin samar da lantarki kan bashin tiriliyan huɗu

Tinubu zai gana da kamfanonin samar da lantarki kan bashin tiriliyan huɗu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai gana da shugabanni na kamfanonin da ke samar da lantarki a ƙasar domin tattaunawa kan bashin naira tiriliyan huɗu da suke bi.

Wata sanarwa da mai magana da yawun Ministan Lantarki Adebayo Adelabu ya fitar ranar Lahadi ta ce gwamnatin tarayya “ta ƙagu ta shawo kan matsalar” bayan ganawar da ministan ya yi da shugaban kamfanonin ranar Talata.

Yayin ganawar, ministan ya tabbatar wa kamfanonin da ake kira Generation Companies (GenCos) cewa gwamnati za ta mayar da hankali wajen wani ɓangare na bashin, in ji sanarwar.

“Akwai buƙatar mu biya wani babban ɓangare na kuɗin kuɗi hannu, idan ya so daga baya sai mu nemi a yi mana lamuni na biyan ragowar nan gaba,” a cewar ministan kamar yadda Bolaji Tunji ya ruwaito cikin sanarwar.

Ta ƙara da cewa za a daddale abin da gwamnatin za ta biya ne yayin ganawar tsakanin shugaban ƙasa da shugabannin kamfanonin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp