Home General Adadin kuɗin shigar Dangote zai kai dala biliyan 30 a shekara mai...

Adadin kuɗin shigar Dangote zai kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa

Fitaccen attajirin Nahiyar Afirka Aliko Dangote ya ce zai samu kuɗin shiga a dukkanin hada-hadar kasuwancisa da ta kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa, dukda yadda harajin Amurka zai shafi kamfanoninshi.

Shugaban rukunin kamfanonin na Dangote ya ce kasuwancinsa da suka haɗa da matatar man fetur mai ƙarfin tace ganga dubu 650 a kullum zai ƙaru da dala biliyan 5 a shekarar 2026.

Adadin kuɗin shigar kamfanonin na Dangote dai a wannan shekarar ya kai dala biliyan 25 abin da ke nufin idan an samu ƙarin dala biliyan 5 zai kama dala biliyan 30 a baɗi.

Shugaban Amurka Donlad Trump ya ware fannin mai da gas daga ƙarin haraji abin da ya sa matatar Dangote ci gaba da shigar da mai  a ƙasar. Baya ga haka Dangote na kai taki ƙasar ta Amurka.

Adadin harajin shigar da kaya da Najeriya ke biyan Amurka ya yi ƙasa da kashi 16 idan aka kwatanta da wanda Algeria ke biyan ƙasar, abin da ya bai wa ƙasar damar hada-hadar kasuwanci fiye da Algeria.

Dangote ya ce ya damu da harajin da Amurka ta sanya, saboda kashi 37 na takin da yake sayarwa na Urea yana zuwa Amurka ne. sai dai sun yi sa a ita ƙasar Algeria an ƙaƙaba mata kashi 30 na haraji.

A gefe guda kuma ana hasashen Dangote zai zama babban mai fitar da siminti a nahiyar Afirka a shekara mai zuwa, inda zai iya kere ƙasar Masar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp