Home General Adadin kuɗin shigar Dangote zai kai dala biliyan 30 a shekara mai...

Adadin kuɗin shigar Dangote zai kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa

Fitaccen attajirin Nahiyar Afirka Aliko Dangote ya ce zai samu kuɗin shiga a dukkanin hada-hadar kasuwancisa da ta kai dala biliyan 30 a shekara mai zuwa, dukda yadda harajin Amurka zai shafi kamfanoninshi.

Shugaban rukunin kamfanonin na Dangote ya ce kasuwancinsa da suka haɗa da matatar man fetur mai ƙarfin tace ganga dubu 650 a kullum zai ƙaru da dala biliyan 5 a shekarar 2026.

Adadin kuɗin shigar kamfanonin na Dangote dai a wannan shekarar ya kai dala biliyan 25 abin da ke nufin idan an samu ƙarin dala biliyan 5 zai kama dala biliyan 30 a baɗi.

Shugaban Amurka Donlad Trump ya ware fannin mai da gas daga ƙarin haraji abin da ya sa matatar Dangote ci gaba da shigar da mai  a ƙasar. Baya ga haka Dangote na kai taki ƙasar ta Amurka.

Adadin harajin shigar da kaya da Najeriya ke biyan Amurka ya yi ƙasa da kashi 16 idan aka kwatanta da wanda Algeria ke biyan ƙasar, abin da ya bai wa ƙasar damar hada-hadar kasuwanci fiye da Algeria.

Dangote ya ce ya damu da harajin da Amurka ta sanya, saboda kashi 37 na takin da yake sayarwa na Urea yana zuwa Amurka ne. sai dai sun yi sa a ita ƙasar Algeria an ƙaƙaba mata kashi 30 na haraji.

A gefe guda kuma ana hasashen Dangote zai zama babban mai fitar da siminti a nahiyar Afirka a shekara mai zuwa, inda zai iya kere ƙasar Masar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp