Home General Mutum 27 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kwara

Mutum 27 sun mutu a hatsarin kwale-kwale a Kwara

Mutum 27 ne suka rasu bayan da kwale-kwalensu ya kife a karamar hukumar Kaiama na jihar Kwara.

Rahotanni sun bayyana cewa fasinjojin na kan hanyar su ne ta komawa gida daga kasuwa a jihar Neja, lokacin da jirginsu ya nitse.

Wani da ya tsira daga hatsarin, ya ce lamarin ya faru ne sakamakon ɗaukar kaya fiye da kima, kamar yadda gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito.

Ya ce iska mai ƙarfi da ta taso musu – ita ma ta taimaka wajen kifar da kwale-kwalen, duk da cewa bai bayyana adadin mutanen da ke cikin jirgin ba.

Shugaban karamar hukumar ta Kaiama, Abdullahi Danladi, wanda ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar don zuwa ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa, ya ce gwamnati ba za ta ci gaba da lamuntar samun hatsuran kwale-kwale da ake yi ba a kowace shekara.

Ya sanar da shirin kafa wani kwamitin da zai ɗabbaka saka rigunan kariya da hana tafiye-tafiye cikin dare da kuma aiwatar da sauran matakai na tsaro.

Hatsarin jirgin ruwan na zuwa ne watanni bakwai bayan samun irinsa da ya lakume rayukan mutane 100 a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp