Mutum 27 ne suka rasu bayan da kwale-kwalensu ya kife a karamar hukumar Kaiama na jihar Kwara.
Rahotanni sun bayyana cewa fasinjojin na kan hanyar su ne ta komawa gida daga kasuwa a jihar Neja, lokacin da jirginsu ya nitse.
Wani da ya tsira daga hatsarin, ya ce lamarin ya faru ne sakamakon ɗaukar kaya fiye da kima, kamar yadda gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito.
Ya ce iska mai ƙarfi da ta taso musu – ita ma ta taimaka wajen kifar da kwale-kwalen, duk da cewa bai bayyana adadin mutanen da ke cikin jirgin ba.
Shugaban karamar hukumar ta Kaiama, Abdullahi Danladi, wanda ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar don zuwa ta’aziyya ga iyalan waɗanda lamarin ya shafa, ya ce gwamnati ba za ta ci gaba da lamuntar samun hatsuran kwale-kwale da ake yi ba a kowace shekara.
Ya sanar da shirin kafa wani kwamitin da zai ɗabbaka saka rigunan kariya da hana tafiye-tafiye cikin dare da kuma aiwatar da sauran matakai na tsaro.
Hatsarin jirgin ruwan na zuwa ne watanni bakwai bayan samun irinsa da ya lakume rayukan mutane 100 a yankin.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1462 days 4 hours 16 minutes 25 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 5 hours 57 minutes 50 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com