Jam’iyyar PDP ta kafa kwamitin shirya babban taronta na ƙasa

Jam’iyyar PDP ta kafa kwamitin da zai shirya babban taron jam’iyyar a ƙarƙashin gwamman Adamawa Amadu Fintiri.

PDP ta ce majalisar zartarwar ta amince da kafa wani ƙarin kwamitin da zai yi nazari a kan tsarin karɓa karɓan muƙamai a jam’iyyar gabanin babban taronta, a ƙarƙashin Gwamnan jihar Bayelsa Douye Diri.

Jamiyyar ta ɗauki wannan mataki ne a yayin zaman majalisar ƙoli da ta gudanar a ranar Talata a birnin Abuja.

A yayin taron, jam’iyyar ta kuma yi Allah wadai da rufe hedikwatarta da hukumar kula da birnin Abuja ta yi, tare da shan alwashin bin kadin matakin.

A ranar Litinin hukumar kula da birnin Abuja, FCTA ta garƙame hedikwatar PDP da aka fi sani da Wadata Plaza saboda rashin biyan harajin ƙasa, lamarin da ya janyo cece ku ce.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1485 days 18 hours 21 minutes 8 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1467 days 20 hours 2 minutes 33 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com