Home General Gwamnatin Kano ta fara biyan tsofaffin kansilolin APC hakkokinsu

Gwamnatin Kano ta fara biyan tsofaffin kansilolin APC hakkokinsu

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da fara biyan kudaden tsofaffin kansilolin da suka yi lokacin tsohuwar gwamnatin APC da Kudi sama da Naira Biliyan 16.

Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’amuran cikin gida na jihar kano Com. Ibrahim Abdullahi waiya ya fita aka raba manema labarai a jihar.

Ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika alƙawarin da ya ɗaukarwa tsofaffin kansilolin da sukai mulki a lokacin gwamnatin Ganduje, na fara biyan haƙƙokin su wanda yace Abdullahi Ganduje ya nuna halin ko in kula dasu lokacin da yake kan mulki.

Waiya ya ƙara da cewa rukunin kansilolin da suka fito daga ƙananan hukumomi 44 daga kuma mazaɓu 484 gaba ɗayan su zasu karɓi haƙƙokin nan ba jimawa ba.

A karan farko dai kansiloli 903 ne suka amfana da naira biliyan ɗaya da miliyan ɗari takwas ₦ 1.8. waɗanda sukai aiki daga shekarar daga 2014 zuwa 2017.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp