Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da fara biyan kudaden tsofaffin kansilolin da suka yi lokacin tsohuwar gwamnatin APC da Kudi sama da Naira Biliyan 16.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai da al’amuran cikin gida na jihar kano Com. Ibrahim Abdullahi waiya ya fita aka raba manema labarai a jihar.
Read Also:
Ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika alƙawarin da ya ɗaukarwa tsofaffin kansilolin da sukai mulki a lokacin gwamnatin Ganduje, na fara biyan haƙƙokin su wanda yace Abdullahi Ganduje ya nuna halin ko in kula dasu lokacin da yake kan mulki.
Waiya ya ƙara da cewa rukunin kansilolin da suka fito daga ƙananan hukumomi 44 daga kuma mazaɓu 484 gaba ɗayan su zasu karɓi haƙƙokin nan ba jimawa ba.
A karan farko dai kansiloli 903 ne suka amfana da naira biliyan ɗaya da miliyan ɗari takwas ₦ 1.8. waɗanda sukai aiki daga shekarar daga 2014 zuwa 2017.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1461 days 22 hours 19 minutes 50 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1444 days 1 minute 15 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com