Jirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga’

Wasu rahotannin sun bayyana cewa an kashe musu mutum 20 sakamakon harin ‘yan bindiga da kuma farmakin da wani jirgin sojin Najeriya ya kai domin fatattakar ‘yan bindigar.

Al’ummar wasu ƙauyuka da ke yankin ƙaramar hukumar Maru a jihar Zamfara da ke arewa maso yammacin Najeriya, sun ka bayyana hakan kamar yadda bbc ta rawaito.

Mazauna yankin sun ce ‘yan bindigar sun sace mutune sama da 50 da ke aikin noma, amma jirgin saman da ya kawo dauki ya kashe wasu daga cikin ‘yan sakai da ke ƙoƙarin korar ‘yan bindigar.

Mazauna unguwar Mani da ke yankin ƙaramar hukumar ta Maru sun ce ‘yan bindigar waɗanda suke kan babura sun kai musu harin da rana a lokacin da ake tsaka da aikin gona.

Mutanen sun ce koda isarsu sai suka fara harbin kan mai uwa da wabi da kuma kama wasu mutanen.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1461 days 21 hours 25 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1443 days 23 hours 7 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com