Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin gobara a ɗaya daga cikin otal ɗin da alhazan ƙasar ke zaune a ciki a Shari Mansur da ke birnin Makka.
Wata sanarwa da hukumar ta fitar yau Asabar, ta ce otal ɗin ya kasance yana ɗaukar mahajjata 484, sai dai ba a samu asarar rayuka ba saboda dukkan alhazan na Mina.
Hukumar agajin gaggawa ta Saudiyya da hukumar gudanarwar otal ɗin ne suka yi ƙoƙarin kashe gobarar.
Shugaban hukumar Alhazai ta Najeriya, Farfesa Abdullahi Saleh Usman ya bayar da umarnin sauyawa alhazan wurin zama lokacin da kai ziyara wurin.
Ya jajantawa waɗanda gobarar ta shafa tare ɗaukar alwashin taimaka musu.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1485 days 14 hours 28 minutes 44 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1467 days 16 hours 10 minutes 9 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com