An yi Jana’izar mutum 10 da ƴar kumar bakin wake ta hallaka a Borno

Rundunar ƴansandan jihar ta tabbatar da harin da wata ƴar ƙunar bakin wake ta kai a babbar kasuwar kifi da ke Konduga, inda ta ce aƙalla mutum 10 sun mutu, duk da wata majiya ta ce aƙalla mutum 20 ne suka mutu, ciki har da ƴan sa-kai da suke taimakon sojoji wajen yaƙin da ƴan ƙungiyar.

A daren Juma’a na 20 ga Yuni, 2025 ne rahotani suka nuna cewa wata ƴar ƙunar bakin waken ta kai harin a garin na Konduga, wanda ke kusa da Maiduguri, babban birnin jihar Borno.

Da yake magana game da harin, mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya yi Allah wadai da harin, sannan ya yi kira ga jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.

An ga wasu hotuna da aka jera gawarwakin waɗanda harin ya rutsa da su a lokacin da ake shirin yi musu jana’iza.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1465 days 7 hours 58 minutes 59 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1447 days 9 hours 40 minutes 24 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com