Rundunar ƴansandan jihar ta tabbatar da harin da wata ƴar ƙunar bakin wake ta kai a babbar kasuwar kifi da ke Konduga, inda ta ce aƙalla mutum 10 sun mutu, duk da wata majiya ta ce aƙalla mutum 20 ne suka mutu, ciki har da ƴan sa-kai da suke taimakon sojoji wajen yaƙin da ƴan ƙungiyar.
Read Also:
A daren Juma’a na 20 ga Yuni, 2025 ne rahotani suka nuna cewa wata ƴar ƙunar bakin waken ta kai harin a garin na Konduga, wanda ke kusa da Maiduguri, babban birnin jihar Borno.
Da yake magana game da harin, mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ya yi Allah wadai da harin, sannan ya yi kira ga jami’an tsaro su ɗauki matakin gaggawa.
An ga wasu hotuna da aka jera gawarwakin waɗanda harin ya rutsa da su a lokacin da ake shirin yi musu jana’iza.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1465 days 7 hours 58 minutes 59 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1447 days 9 hours 40 minutes 24 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Report By: PRNigeria.com