Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki don hana sake faruwar kisan mutane a jihar bayan kisan wasu ƴan asalin jihar Kaduna a ƙaramar hukumar Mangu da ke jihar.

A makon jiya ne dai aka kashe wasu matafiya 12 ƴan Zaria, da ba su ji ba su gani ba, wani abu da ya janyo Allah-wadai daga ɓangarori daban-daban.

Joyce Ramnav, ita ce kwamishiniyar watsa labarai a jihar ta Filato, ta bayyanawa BBC cewa burinsu shi ne su nuna wa duniya cewa Filato jiha ce mai son zaman lafiya, mai maraba da mutane.

Ta ce, “jami’an tsaron sun kama mutum 22, kuma idan allah ya yarda gwamnati za ta ɗauki matakin domin a tabbatar an hukunta waɗannan mutane.”

Ta ce yanzu gwamnati na jiran sakamakon bincike ne da ƴansandan jihar ke gabatarwa, “kafin mu san matakin da za mu ɗauka na gaba.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1470 days 23 hours 21 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1453 days 1 hour 3 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com