Home General Gwamnatin jihar Kano ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan asalin jihar a...

Gwamnatin jihar Kano ta yi Alla-wadai da kisan ‘yan asalin jihar a Benuwai

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf ya yi Alla-wadai da kisan matasa ‘yan asalin jihar a garin makurdi dake jihar Benuwai.
Wannan na cikin wata takardar sanarwa da Mai Magana da yawan Gwamnan kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, Sanusi Bature Dawakin Tofa  ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano.
Sanarwar ta ce lamarin ya auku ga Matasan ne da misalin karfe 11: na daren litinin wanda kawo yanzu ba a kai ga gano wadanda suka aikata wannan aika-aikar ba.
Cikin bakin cikin gwamnan Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana kisan na rashin imani matsayin rashin hankali, wanda kuma ba za a lamunta ba.
Tun da fari dai an ruwaito matasan biyu da suka haɗar da Barham Sulaiman da Jamilu Ahmad ƴan asalin unguwa uku ne a jihar Kano.
Daga bisani sanarwa ta ce Gwamnan zai jagorancin wata tawagar ciki har da iyayen matasan domin gudanar da Jana’izarsu a babban masallacin ƙasa dake birnin Abuja.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp