Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba kabir Yusuf ya yi Alla-wadai da kisan matasa ‘yan asalin jihar a garin makurdi dake jihar Benuwai.
Wannan na cikin wata takardar sanarwa da Mai Magana da yawan Gwamnan kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano.
Sanarwar ta ce lamarin ya auku ga Matasan ne da misalin karfe 11: na daren litinin wanda kawo yanzu ba a kai ga gano wadanda suka aikata wannan aika-aikar ba.
Cikin bakin cikin gwamnan Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayyana kisan na rashin imani matsayin rashin hankali, wanda kuma ba za a lamunta ba.
Tun da fari dai an ruwaito matasan biyu da suka haɗar da Barham Sulaiman da Jamilu Ahmad ƴan asalin unguwa uku ne a jihar Kano.
Daga bisani sanarwa ta ce Gwamnan zai jagorancin wata tawagar ciki har da iyayen matasan domin gudanar da Jana’izarsu a babban masallacin ƙasa dake birnin Abuja.
Kidnapped School Children
Yauri FGC Students, Kebbi1470 days 23 hours 11 minutes 56 seconds,
Baptist School Students, Kaduna
1453 days 53 minutes 21 seconds
Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021
Report By: PRNigeria.com