INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a Najeriya

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC, ta tsaida ranar 16 ga watan Agustan wannan shekarar, don gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a jihohi 12 na ƙasar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan, yayin wata ganawa da shugabannin jam’iyyu da ya yi a Abuja a jiya Alhamis.

Ya ce an samu giɓin kujerun ne, sakamakon mutuwa da kuma hukuncin kotu da ya soke sakamakon wasu zaɓuka.

Za a gudanar da zaɓen ne a mazaɓu 16 da suka haɗa da sanatoci biyu da ƴan majalisar tarayya 5 sai kuma ƴan majalisar dokoki 9.

Shugaban na INEC ya ce hukumar za ta tura da jami’anta dubu 30 da ɗari 451 don gudanar da zaɓukan da mutane miliyan 3 da dubu dari 553 da ɗari 659 za su kaɗa kuri’a a rumfunar zaɓe dubu 6 da ɗari 987.

Sai dai ya ce ba za su gudanar da zaɓe a mazaɓar Khana ll da ke jihar Rivers bisa dokar taɓaci da aka sanya, da kuma mazaɓar Talata Mafara ta Kudu da ke jihar Zamfara, sakamakon rashin kammala shari’ar da ake yi a kai.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1471 days 8 hours 39 minutes 9 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1453 days 10 hours 20 minutes 34 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com