Home General Tinubu zai saka hannu a sabuwar dokar haraji da ta yamutsa hazo

Tinubu zai saka hannu a sabuwar dokar haraji da ta yamutsa hazo

Shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin sauya tsarin haraji na ƙasar a yau Alhamis, a wani mataki da ake sa ran zai sauya tsarin tattara haraji da kuma inganta yanayin kasuwanci a Najeriya.

Sanarwar da fadar shugaban ƙasar ta fitar ta hannun mai taimaka masa kan yaɗa labaru, Bayo Onanuga ta ce sabbin dokokin huɗu sun haɗa da dokar haraji ta ƙasa da dokar tafiyar da lammuran haraji da dokar kafa hukumar haraji ta Najeriya da kuma dokar kafa ma’aikatar kula da hukumomin tattara haraji ta Najeriya.

Majalisar Dokoki ta kasa ce za ta amince da su bayan shawarwari da dama daga masu ruwa da tsaki.

Sabbin dokokin harajin na Najeriya sun tayar da ƙura sosai a lokacin da shugaban ƙasar ya gabatar da su ga majalisar dokokin ƙasar, lamarin da ya kai ga dakatar da tattaunawa a kan su a zauren majalisar.

Tun da farko gwamnonin jihohin ƙasar da majalisar kula da tattalin arziƙi ta Najeriya da ƙungiyoyi sun buƙaci a sake duba dokar kafin sake gabatar da ita.

Daga baya gwamnonin jihohin ƙasar sun gudanar da gyare-gyare kan dokar tare da gabatar wa shugaban ƙasa, wanda ya amince da su kafin majalisar dokokin ƙasar ta ci gaba da muhawara.

Majalisar dokokin ƙasar ta ce a halin yanzu an gyara duk wasu ɓangarori da suka haifar da tayar da jijiyoyin wuya.

Sai dai har yanzu al’umma da dama ba su da cikakkiyar masaniyar abubuwan da dokokin suka ƙunsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp