Home General INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a...

INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a Najeriya

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC, ta tsaida ranar 16 ga watan Agustan wannan shekarar, don gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a jihohi 12 na ƙasar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan, yayin wata ganawa da shugabannin jam’iyyu da ya yi a Abuja a jiya Alhamis.

Ya ce an samu giɓin kujerun ne, sakamakon mutuwa da kuma hukuncin kotu da ya soke sakamakon wasu zaɓuka.

Za a gudanar da zaɓen ne a mazaɓu 16 da suka haɗa da sanatoci biyu da ƴan majalisar tarayya 5 sai kuma ƴan majalisar dokoki 9.

Shugaban na INEC ya ce hukumar za ta tura da jami’anta dubu 30 da ɗari 451 don gudanar da zaɓukan da mutane miliyan 3 da dubu dari 553 da ɗari 659 za su kaɗa kuri’a a rumfunar zaɓe dubu 6 da ɗari 987.

Sai dai ya ce ba za su gudanar da zaɓe a mazaɓar Khana ll da ke jihar Rivers bisa dokar taɓaci da aka sanya, da kuma mazaɓar Talata Mafara ta Kudu da ke jihar Zamfara, sakamakon rashin kammala shari’ar da ake yi a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp