Home General INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a...

INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a Najeriya

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC, ta tsaida ranar 16 ga watan Agustan wannan shekarar, don gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a jihohi 12 na ƙasar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan, yayin wata ganawa da shugabannin jam’iyyu da ya yi a Abuja a jiya Alhamis.

Ya ce an samu giɓin kujerun ne, sakamakon mutuwa da kuma hukuncin kotu da ya soke sakamakon wasu zaɓuka.

Za a gudanar da zaɓen ne a mazaɓu 16 da suka haɗa da sanatoci biyu da ƴan majalisar tarayya 5 sai kuma ƴan majalisar dokoki 9.

Shugaban na INEC ya ce hukumar za ta tura da jami’anta dubu 30 da ɗari 451 don gudanar da zaɓukan da mutane miliyan 3 da dubu dari 553 da ɗari 659 za su kaɗa kuri’a a rumfunar zaɓe dubu 6 da ɗari 987.

Sai dai ya ce ba za su gudanar da zaɓe a mazaɓar Khana ll da ke jihar Rivers bisa dokar taɓaci da aka sanya, da kuma mazaɓar Talata Mafara ta Kudu da ke jihar Zamfara, sakamakon rashin kammala shari’ar da ake yi a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp