Home General INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a...

INEC ta tsaida ranar gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a Najeriya

Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta a Najeriya INEC, ta tsaida ranar 16 ga watan Agustan wannan shekarar, don gudanar da zaɓukan cike gurbin ƴan majalisu a jihohi 12 na ƙasar.

Shugaban hukumar ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya bayyana hakan, yayin wata ganawa da shugabannin jam’iyyu da ya yi a Abuja a jiya Alhamis.

Ya ce an samu giɓin kujerun ne, sakamakon mutuwa da kuma hukuncin kotu da ya soke sakamakon wasu zaɓuka.

Za a gudanar da zaɓen ne a mazaɓu 16 da suka haɗa da sanatoci biyu da ƴan majalisar tarayya 5 sai kuma ƴan majalisar dokoki 9.

Shugaban na INEC ya ce hukumar za ta tura da jami’anta dubu 30 da ɗari 451 don gudanar da zaɓukan da mutane miliyan 3 da dubu dari 553 da ɗari 659 za su kaɗa kuri’a a rumfunar zaɓe dubu 6 da ɗari 987.

Sai dai ya ce ba za su gudanar da zaɓe a mazaɓar Khana ll da ke jihar Rivers bisa dokar taɓaci da aka sanya, da kuma mazaɓar Talata Mafara ta Kudu da ke jihar Zamfara, sakamakon rashin kammala shari’ar da ake yi a kai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp