Home General Ba mu warware rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar ba – Umar Fintiri

Ba mu warware rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar ba – Umar Fintiri

Sakamakon mahawara mai zafi da kuma sukar da ta biyo bayan sabuwar dokar masarautun jihar Adamawa dake Najeriya, wadda aka ce ta tube rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar, gwamnan jihar Umaru Fintiri ya ce ba haka lamarin yake ba.

Fintiri wanda ya yi watsi da zargin cewar an yi dokar ce domin musgunawa wasu masu rike da sarautar gargajiya a jihar, cikin su harda tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ya ce babu wani mai sarauta da aka sauke yanzu haka.

Gwamnan ya ce Lamidon Adamawa ne zai fayyace matsayin sarautar Atiku na Wazirin Adamawa da kuma makomarsa kamar yadda sabuwar dokar masarautun jihar ta tanada.

Fintiri ya ce Wazirin Adamawa sarauta ce kawai, amma baya daga cikin masu zaben Sarki ko kuma zama mukami na biyu bayan Lamidon Adamawa.

Gwamnan ya ce Masarautun jihar ce za su tantance masu zaben sarki da kuma ƴan majalisar sa daidai da sabuwar dokar da aka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp