Home General Ba mu warware rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar ba – Umar Fintiri

Ba mu warware rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar ba – Umar Fintiri

Sakamakon mahawara mai zafi da kuma sukar da ta biyo bayan sabuwar dokar masarautun jihar Adamawa dake Najeriya, wadda aka ce ta tube rawanin Wazirin Adamawa Atiku Abubakar, gwamnan jihar Umaru Fintiri ya ce ba haka lamarin yake ba.

Fintiri wanda ya yi watsi da zargin cewar an yi dokar ce domin musgunawa wasu masu rike da sarautar gargajiya a jihar, cikin su harda tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar, ya ce babu wani mai sarauta da aka sauke yanzu haka.

Gwamnan ya ce Lamidon Adamawa ne zai fayyace matsayin sarautar Atiku na Wazirin Adamawa da kuma makomarsa kamar yadda sabuwar dokar masarautun jihar ta tanada.

Fintiri ya ce Wazirin Adamawa sarauta ce kawai, amma baya daga cikin masu zaben Sarki ko kuma zama mukami na biyu bayan Lamidon Adamawa.

Gwamnan ya ce Masarautun jihar ce za su tantance masu zaben sarki da kuma ƴan majalisar sa daidai da sabuwar dokar da aka yi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp