Home General Bello Turji ya kashe ƴan sa-kai sama da 40 a Zamfara

Bello Turji ya kashe ƴan sa-kai sama da 40 a Zamfara

Rahotannin na bayyana cewa guda cikin manyan ’yan bindigar da suka addabi Najeriya, Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a wani harin kwanton bauna da ya kai a jihar Zamfara ranar Lahadi.

Majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa an kai harin ne a kusa da Rugar Chida, wani kauyen da mahaifin Bello Turjin ke rike da sarautar gargajiya.

An dai yi wa jami’an da ke tafiya a cikin motoci biyu da babura kwanton baunar ne a yankin wanda ya shafe mako biyu babu sabis din waya saboda aikin da sojoji suke a ciki.

Wata majiya a yankin ta tabbatar wa Aminiya cewa harin ya daga musu hankali matuka kuma an shirya shi yadda ya kamata.

Majiyar ta ce, “An mamaye su. Bello Turji da yaransa sun kashe mutum 40 daga cikinsu sannan suka kwace ababen hawan da suke kai.

“Turji ya ji dadin harin sosai musamman saboda Bashar Maniya na cikin wadanda aka kashe, wanda tun a baya dama babban abokin hamayyarsa ne kafin ya tuba daga ta’addancin,” in ji majiyar.

A cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, an ga Bello Turji yana murna tare da nuna gawarwakin mutanen, ciki har da ta Bashar Maniya, yana rera wakokin cin nasara.

“Wannan ce gawar Kwamandan da ya jagoranci harin,” kamar yadda aka jiyo Turjin yana bayyanawa a cikin bidiyon.

Daga bisani dai an kwaso gawarwakin mutanen tare da gudunmawar sojojin sama, yayin da wadanda suka jikkata kuma aka garzaya da su asibiti.

Wani jami’in tsaro da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi da abin takaici da za a iya kauce masa matukar ana aiki tare tsakanin jami’an tsaro da mutanen gari.

Bayanai dai sun nuna gabanin kisan mayakan, an kashe ’yan bindiga yaran Bello Turji sama da 30 a wata ba-ta-kashi da aka yi tsakanin yaran Turjin da na Maniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp