Shugaba Tinubu ya mika ta’aziyyar Alhaji Aminu Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta’aziyarsa ta rasuwar Alhaji Aminu Ɗantata, attajirin ɗankasuwa da ya rasu a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, wanda ya rasu yana da shekara 94 a duniya.

Tinubu ya bayyana rasuwar hamshaƙin ɗankasuwar, wanda aka binne a ƙasar Saudiyya a matsayin “rashi ga ƙasar baki ɗaya’.

Tinubu ya yaba da gudunmuwar da marigayin ya bayar wajen ciyar da Najeriya gaba, “musamman a ɓangaren ilimi da kiwon lafiya,” kamar yadda sanarwar da mai magana da yawun shugaban, Bayo Onanuga ya fitar.

Tinubu ya ce, “mun yi rashi na babban ɗankasuwa, mai kishin ƙasa, kuma dattijon arziki wanda ya ya taimaka wajen gina ƙasarmu Najeriya.”

Tinubu ya ce za a riƙa tuna Ɗantata a matsayin ɗankasuwa mai sanin ya kamata wanda ya bayar da gudunmuwa wajen haɗin kan ƙasa ta hanyar kasuwancinsa da ayyukan jinƙai, “wanda amfanar da ƴan Najeriya da ba za su ƙirbu ba.”

A ƙarshe Tinubu ya jajanta wa iyalan marigayin tare gwamnati da al’ummar Kano baki ɗaya bisa.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1473 days 17 hours 28 minutes 41 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1455 days 19 hours 10 minutes 6 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com