Home General Sojojin Najeriya sun kai farmakin ramuwar gayya kan ƴan bindiga a Neja

Sojojin Najeriya sun kai farmakin ramuwar gayya kan ƴan bindiga a Neja

Dakarun Sojin Saman Najeriya sun ce sun ƙaddamar da gagarumin farmakin sama kan sansanonin ‘yan bindiga a jihar Neja a ranakun Laraba da Alhamis, a wani yunƙuri na kawar da ƴan fashin da suka kai hari kan dakarun ƙasar a baya-bayan nan.

Wata sanarwa da rundunar sojin saman ta wallafa a shafinta na sada zumunta ta ce an kai harin ne ƙarƙashin shirin FANSAN YAMMA “domin kawar da barazanar tsaro da ‘yan ta’adda ke haifarwa.

“A ranar 26 ga watan Yuni, bayan samun bayanan sirri, rundunar sojin saman Najeriya, bayan haɗa gwiwa da sauran jami’an tsaro ta gano ayyukan ƴan bindiga da suka hada da satar shanu a yankin Kakihun da Kumbashi,” in ji sanarwar wadda ta samu sa hannu daraktan yaɗa labarai na rundunar Air Commodore Ehimen Ejodame.

“Nan take rundunar ta ƙaddamar da hare-haren da suka yi sanadin kashe ƴan fashin daji da dama, lalata kayan aikinsu da kuma hana su haɗuwa,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

A cikin makon nan ne aka samu rahotannin da suka ce ƴan fashin daji a jihar ta Neja, arewa maso tsakiyar Najeriya sun kai samame a wasu sansanonin sojin Najeriya inda suka kashe jami’an soji “aƙalla 17”.

Wata sanarwa da rundunar sojin ƙasa ta Najeriyar ta fitar ta tabbatar da kai harin sai dai ba ta yi bayani kan yawan sojojin da suka rasa rayukansu ba sanadiyyar farmakin.

Neja na cikin jihohin Najeriya masu fama da matsalar tsaro, inda ƴan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka da dama, lamarin da ya haifar da asarar ɗimbin rayuka da kawo cikas ga ayyukan tattalin arziƙi

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp