Home Labarai Gwamnatin Filato ta zargi jami’an tsaro da rashin kama maharan jihar

Gwamnatin Filato ta zargi jami’an tsaro da rashin kama maharan jihar

Gwamnatin jihar Filato da ke tsakiyar Najeriya ta zargi jami’an sojojin ƙasar da sakaci wajen rashin kama maharan da suka kashe mutum 27 a garin Tahoss na yankin ƙaramar hukumar Riyom.

A farkon makon nan ne wasu mahara ɗauke da makamai suka auka wa garin tare da halaka mutum 27 da raunata wasu.

Yayin wata hira da gidan talbijin na Channels ranar Juma’a ta cikin shirin ”The Morning Brief” kwamishiniyar yaɗa labaran jihar, Joyce Ramnap ta ce sojojin da ke yankin sun nuna sakaci wajen rashin kama ko da mutum guda cikin maharan, duk kuwa da kasancewar sojojin a kusa da garin.

Kwamishiniyar ta ce garin da aka kai harin na kusa da shingen binciken ababen hawa da sojoji ke gudanarwa.

“Akwai shingen binciken ababen hawa na sojoji, wanda bai fi tazarar mita 200 daga wurin da lamarin ya faru, kuma daga bayanan da muka samu ba wanda suka kama, kuma ba su kashe kowa ba”.

“Garin nan ba wani gari ba ne mai nisa da za a ce kafin a kai inda suke an yi musu lahani, suna kusa da titi,” in ji ta.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp