Kotu Ta Kori Karar Da APC Ta Shigar Domin Hana Kudaden Kananan Hukumomi

Babbar Kotun Tarayya mai lamba 3 da ke Kano ƙarƙashin jagorancin Mai shari’a Simon Amobeda ta kori karar da jam’iyyar APC da Hon. Abdullahi Abbas da Hon. Aminu Aliyu Tiga suka shigar domin hana biyan kuɗaɗen kananan hukumomi a Kano.

Masu ƙarar sun nemi hakan ne bisa hujjar cewa an saba umarnin kotu da ya hana gudanar da zaɓen.

A zaman kotun lauyan masu ƙara ya nemi a jingine shari’ar, amma lauyan gwamnatin Kano ya nemi a kori ta tare da biyan diyya.

A karshe Kotun dai ta yanke hukunci da korar karar baki ɗaya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com