Home Labarai An samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga – Ribadu

An samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga – Ribadu

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce an samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴanbindiga har ma da rikice-rikice tsakanin al’ummomi a yankin arewacin ƙasar cikin shekaru biyu da suka wuce karkashin gwamnatin shugaba Tinubu – idan aka kwatanta da gwamnatin da ta gabata.

Ya bayar da misalin cewa an kashe mutum 1,192 sannan an sace sama da 3,348 a jihar Kaduna a gwamnatin da ta shuɗe, yayin da sama da mutane 5,000 suka rasa rayukansu a jihar Benue a wannan lokaci.

Ribadu ya bayyana haka ne a yau Talata yayin jawabi a taron masu ruwa da tsaki na arewacin Najeriya wanda aka gudanar a jihar Kaduna.

Ya ce nasarar da aka samu a yaƙi da rashin tsaro ya samo asali ne sakamakon umarnin da shugaba Tinubu ya bai wa jami’an tsaro kan bin tsarin tabbatar da tsaro na bai-ɗaya.

Ya ƙara da cewa an samu nasarar sakin mutum 11,259 waɗanda aka yi garkuwa da su a watan Mayu kaɗai – a wasu samame daban-daban da sojojin Najeriya suka kai a arewa maso yamma.

Ribadu ya kuma bayyana cewa jami’an tsaro sun kashe shugabannin ƴanbindiga da mambobinsu da dama a jihohin Zamfara da Kaduna da kuma Katsina.

Mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan tsaro ya yaba wa gwamnan jihar Kaduna Uba Sani kan amfani da hanyoyi daban-daban wajen shawo kan matsalar tsaro a kudancin jihar da Birnin Gwari har ma da wasu yankuna da ke fama da matsalar tsaro a faɗin jihar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp