Home Labarai Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya

Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya

Shugabn Nijeriya Bola Tinubu ya karawa shugaban hukumar hana fasa kwauri ta kasa (Custom) Bashir Adewale Adeniyi wa’adin aiki na shekara guda.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da wa’adin aikin nasa zai kare karshen wata mai kamawa wato 31 ga watan Agustan 2025.

Ta cikin wata sanarwa daga Fadar Shugaban Ƙasa da Bayo Onanuga, Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, ya sanya wa hannu, wadda ta ce ƙarin wa’adin na da nufin bai wa Adeniyi damar kammala sauye-sauyen da ake aiwatarwa tare da cika manyan manufofin gwamnatin Bola Tinubu.

Ayyukan  da ake son kammalawa sun haɗa da sabunta tsarin aikin Hukumar Kwastam, aiwatar da tsarin National Single Window Project, da kuma cika alƙawarin da Najeriya ta ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar ciniki ta nahiyar Afirka (AfCFTA).

Shugaba Tinubu ya yabawa Adeniyi bisa “ƙwazo da ya nuna wajen jagoranci da da kuma hidimatawa,” yana mai bayyana tabbacin cewa ƙarin wa’adin zai ƙarfafa rawar da Hukumar Kwastam ke takawa a fannin sauƙaƙe cinikayya, haɓaka kuɗaɗen shiga, da kuma tsaro a kan iyakoki Nijeriya.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp