Home Labarai Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya NEMA ta ce mamakon ruwan sama da yin gine-gine kan magunan ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri.

A ranar Laraba ne aka samu rahotonni ambaliya a wasu unguwannin birnin Maiduguri da yankin ƙaramar hukumar Jere sakamakon ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da aka shafe tsawo sa’a uku ana tafkawa a birnin.

Cikin wata sanarwa da shugaban hukumar NEMA, Zubaida Umar ta wallafa a shafinta na Facebook ta danganta ambaliyar da rashin bin tsarin gine-gine.

”ambaliyar na da alaƙa da mamakon ruwan sama da aka samu a birnin da kuma rashin kula da kwalbatoci da yin gine-gine kan hanyoyin da ruwa ke bi”, in ji shugabar ta NEMA.

Hukumar ta NEMA ta ce jami’anta tare da haɗin gwiwar sauran hukumomi sun taimaka wajen ceto mutanen da ambaliyar ta rutsa da su tare da rage illar ambaliyar.

Ambaliyar na zuwa ne ƙasa da shekara guda bayan wata mummunar ambaliyar da ta auka wa yankin, wadda ta yi sanadiyyar raba fiye da mutum miliyan guda da muhallansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp