Home Labarai Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya

Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya

Shugabn Nijeriya Bola Tinubu ya karawa shugaban hukumar hana fasa kwauri ta kasa (Custom) Bashir Adewale Adeniyi wa’adin aiki na shekara guda.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da wa’adin aikin nasa zai kare karshen wata mai kamawa wato 31 ga watan Agustan 2025.

Ta cikin wata sanarwa daga Fadar Shugaban Ƙasa da Bayo Onanuga, Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan Harkokin Bayani da Tsare-tsare, ya sanya wa hannu, wadda ta ce ƙarin wa’adin na da nufin bai wa Adeniyi damar kammala sauye-sauyen da ake aiwatarwa tare da cika manyan manufofin gwamnatin Bola Tinubu.

Ayyukan  da ake son kammalawa sun haɗa da sabunta tsarin aikin Hukumar Kwastam, aiwatar da tsarin National Single Window Project, da kuma cika alƙawarin da Najeriya ta ɗauka a ƙarƙashin yarjejeniyar ciniki ta nahiyar Afirka (AfCFTA).

Shugaba Tinubu ya yabawa Adeniyi bisa “ƙwazo da ya nuna wajen jagoranci da da kuma hidimatawa,” yana mai bayyana tabbacin cewa ƙarin wa’adin zai ƙarfafa rawar da Hukumar Kwastam ke takawa a fannin sauƙaƙe cinikayya, haɓaka kuɗaɗen shiga, da kuma tsaro a kan iyakoki Nijeriya.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp