Home Labarai KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta

KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta

Hukumar Kula da zirga-zirgar ababawan hawa ta jihar Kano (KAROTA) na shirin yin hadin gwiwa da KACHMA don inganta lafiyar ma’aikatanta

Wannan na cikin wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a  na hukumar Abubakar Ibrahim Sharada ya fitar ya kuma aikewa PRNigeria wadda ta cewa, Manajan Daraktan Hukumar Hon. Injiniya Faisal Mahmud Kabir ne ya bayyana aniyar hukumar na yin hadin gwiwar yayin da yake karbar bakuncin sakatariyar zartawar hukumar ta (KACHMA) Dr Rahila Muktar a shalkwatar hukumar karota.

Hon. Faisal Mahmud ya bayyana cewa lafiyar ma’aikatan KAROTA na daga cikin abubuwan da yake baiwa muhimmanci sosai, ganin irin hadurran da ke tattare da ayyukan da suke gudanarwa.

Shugaban KAROTA ya bayyana cewa hukumar na da shirin gyara da fadada asibitin ma’aikatan da ke cikin hukumar domin ya kai ga ingantaccen mataki na aiki.

Ya yaba wa Sakatariyar Zartarwa ta KACHMA bisa wannan ziyara, inda ya tabbatar da cewa za a samu kyakkyawar hulɗa wacce za ta haifar da sakamako mai amfani.

Tun da farko, Dr Rahila Muktar ta bayyana cewa ziyararta KAROTA na da nufin kawo gudunmawar kiwon lafiya daga KACHMA har gida ga ma’aikatan hukumar.

haka kuma ta nuna jin daɗinta bisa kokarin da shugabannin KAROTA suka yi wajen samar da kayayyakin kiwon lafiya a asibitin ma’aikatan su.

Dr Rahila ta tabbatar da cewa KACHMA za ta ba da goyon baya wajen tallafa wa asibitin KAROTA domin ya kai wani mataki na ci gaba da inganci.

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp