Home Labarai Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Tsohon ɗan jamalisar dattawan Najeriya mai wakiltar Kogi ta Yamma ya koma jam’iyyar haɗakar ADC bayan ficewarsa daga PDP.

Cikin wani bidiyo da ya wallafa a shafinsa na X, an ga yadda Dino Melaye ya karɓi katin jam’iyyar ADC daga hannun jagororin jam’iyyar na ƙaramar hukumarsa.

Tun da farko a yau ne Dino Melaye ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP bayan ya rubuta wa jagororin jam’iyyar na mazaɓarsa ta Aiyetoro Gbede wasiƙar ficewarsa daga jam’iyyar.

A cikin wasiƙar Melaye ya bayyana dalilan kasawar jam’iyyar wajen magance matsalolin da ke damunta.

”Matakin ya zama wajibi saboda gazawar jam’iyyar wajen ceto yan Najeriya daga cikin kuncin da ƙasarmu ke ciki”, kamar yadda wasiƙar ta bayyana.

Tsohon ɗan takarar gwamnan jihar Kogin na jam’iyyar PDP ya ce ya ɗauki matakin ne bayan dogon nazari kan halin da jam’iyyar ke ciki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp