Home General Gwamnonin PDP na taro a Zamfara

Gwamnonin PDP na taro a Zamfara

Gwamnonin jam’iyyar PDP a Najeriya na gudanar da wani taro a jihar Zamfara domin tattaunawa kan yunƙurinsu na “ɗaukar matakai masu muhimmanci”.

Taron zai fara ne daga yau Juma’a bayan hallarar gwamnonin, inda ake sa ran tattaunawa kan muhimman batutuwa a gobe Asabar.

A cikin sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ya bayyana cewa, taron na nufin tattauna muhimman batutuwan siyasa da gwamnonin ke fuskanta a halin yanzu.

PDP, wadda ita ce babbar jam’iyyar adawa a Najeriya na fuskantar ƙalubale na rikicin cikin gida da kuma ficewar wasu daga cikin manyan ƴaƴanta, ko dai zuwa jam’iyyar APC mai mulki ko kuma wadanda ke alaƙanta kansu da haɗakar ƴan adawa waɗanda suka tare a jam’iyyar ADC.

Hakan na faruwa ne gabanin babban zaɓen ƙasar na 2027. inda ƴan siyasa a kasar ke ci gaba da shiri, duk kuwa da gargadin da hukumar zaɓen ƙasar mai zaman kanta ta ƙasar ta yi kan fara harkokin siyasa gabanin lokaci.

A cikin sanarwar da gwamnan ya fitar ya ce “taron zai mayar da hankali kan batutuwan da suka shafi haɗin kan jam’iyyar da kuma shirin bunƙasa ci gaban jihohi, musamman a lokacin da jam’iyyar ke shirin gudanar da babban taronta na kasa a garin Ibadan, a ranakun 15 da 16 ga Nuwamba, 2025.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp