Sojoji sun hallaka ’yan fashi 7 a Katsina

Gwamnatin Jihar Katsina, ta ce dakarun sojin Najeriya sun kashe ’yan fashi bakwai a jihar.

 

Ya kara da cewa samamen ya ɗauki sama da awa biyu a ranar Alhamis, bayan samun bayanan sirri cewa ’yan fashin sun kai hari ƙauyen Baba.

Wannan lamari ya faru ne kwanaki kaɗan bayan wani hari da ’yan fashi suka kai  wani masallaci.

Harin ya yi sanadin salwantar rayukan sama da mutane 30, rahotanni kuma na cewa adadin ya kai kusan 50.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com