Home Labarai Fadar shugaban ƙasa ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan Talauci

Fadar shugaban ƙasa ta yi watsi da rahoton Bankin Duniya kan Talauci

Fadar shugaban ƙasa ta maida martani kan rahoton Bankin Duniya da ya ce mutane miliyan 139 na rayuwa cikin talauci a Najeriya, inda ta ce ƙididdigar ba ta nuna hakikanin halin da ake ciki a ƙasar ba.

A cewar fadar shugaban ƙasa, Bankin Duniya ya yi amfani da ƙa’idar duniya wadda ke ɗaukar duk wanda ba ya samun sama da dala $2.15 a rana a matsayin talaka.

Wannan ƙa’ida an kafa ta ne tun shekarar 2017, kuma idan aka fassara ta zuwa kuɗin Najeriya a yau, ta kai kusan Naira 100,000 a wata fiye da sabon mafi ƙarancin albashi na Naira 70,000 kenan.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Fadar shugaban ƙasa ta fitar wanda Sunday Dare, mai magana da yawun shugaban ƙasa ya fitar a shafinsa na X.

‘Bayanan da Bankin Duniya ya dogara da su tsofaffi ne tun daga shekarar 2018/2019, kuma ba su haɗa da tattalin arzikin yanzu ba. Saboda haka, gwamnati ta bayyana cewa wannan adadi misali ne na ƙididdigar duniya, ba ainihin yanayin da ake ciki a shekarar 2025 ba.”

A cewar fadar shugaban ƙasa, abin da ya fi muhimmanci shi ne hanyar da ake bi wajen farfaɗo da tattalin arzikin ƙasa, amma kuma Bankin Duniya ta ce sauye-sauyen Tinubu ba su rage talauci ba.

Ta ce “gwamnatin Shugaba Tinubu tana mai da hankali ne wajen rage wahalar tattalin arziki ta hanyar shirye-shirye na musamman kamar tallafin kuɗi ga talakawa, da bashin karatu na ɗalibai, da sauransu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp